Isa ga babban shafi
Senegal

Mawaƙiya Rihanna ta ja hankalin duniya kan ilimi

Shahararriyar mawakiyar nan ta Amurka Rihanna ta buƙaci jama’a da kada su karaya a yunƙurin bunƙasa ilimi har sai dukkanin yara sun samu karatu a fadin duniya.

Mawakiya Rihanna tare da shugaban Faransa Emmanuel Macron a wurin taron bunkasa ilimi na Global Partnership for Education a Dakar.
Mawakiya Rihanna tare da shugaban Faransa Emmanuel Macron a wurin taron bunkasa ilimi na Global Partnership for Education a Dakar. REUTERS/Philippe Wojazer
Talla

Rihanna ta faɗi haka ne lokacin da ta bayyana tare da shugaban Faransa Emmanuel Macron a wurin taron gidauniyar bunƙasa lilimi a Dakar na ƙasar Senegal.

Haka nan kuma mawaƙiyar ta yi kira ga shugabannin ƙasashen yammacin duniya da firaministan Burtaniya Theresa May su tallafa wa gidauniyar.

Shugaba Macron na Farnsa ya bayyana ilimi a matsayin makamin yaki da ra’ayin riƙau da rikice-rikicen da ke addabar yammacin nahiyar Afirka.

Ya kuma yi alƙawari bayar da Yuro miliyan 200 a matsayin tallafi ga gidauniyar da ta shirya taron.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.