Erdogan na ziyara a kasashen Afrika
Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan ya yaba da nasarar kulla yarjejeniyoyi da hukumomin Algeria a ziyarar da ya fara ta kasashen nahiyar Afirka.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban yace yarjejeniyoyin, zasu bai wa kasashen damar bunkasa harkokin kasuwanci da kuma kare masu zuba jari.
Erdogan yace Turkiy na kallon Algeria a matsayin kasar da ke kan gaba wajen samun kwanciyar hankalin siyasa da kuma habakar tattalin arziki a Afirka.
Ana saran shugaban ya ziyarci kasashen Mauritania, Senegal da kuma Mali.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu