Isa ga babban shafi
Masar

Sojin Masar sun hallaka 'yan bindiga 36

Ma’aikatar tsaron Masar ta ce dakarunta sun kashe ‘yan bindiga 36 yayin da wasu dakarun kasar uku suka hadu da ajalinsu a cigaba da yakin da suke yi domin raba yankin Sinai da ‘yan bindiga.

Wasu dakarun sojin Masar yayin rangadi a arewacin birnin Sinai na kasar da ake zargin 'yan bindiga na boyewa a wajen.
Wasu dakarun sojin Masar yayin rangadi a arewacin birnin Sinai na kasar da ake zargin 'yan bindiga na boyewa a wajen. AFP
Talla

As ranar 9 ga watan fabarairu ne shugaban kasar Abdul Fatah Al-sisi ya bayar da umurnin kaddamar da mummunan farmaki domin murkushe ‘yan ta’adda a wannan yanki da ke arewacin kasar.

Sanarwar Rundunar sojin kasar ta ce sun kuma kwace wasu tarin makamai a sumamen da suka kai arewa da tsakiya da kuma arewacin Sinai.

Haka zalika Sanarwar ta ce kawo yanzu akwai kuma kimanin mutane 345 da aka kame kan zargin hannu a kungiyoyin 'yan bindigar yayin farmakin da suka kaddamar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.