Yan Majalisu sun jikirta batun tsige shugaban Zambia
Majalisar dokokin Zambia ta jinkirta shirin tsige shugaban kasa Edgar Lungu saboda zargin da take masa na taka kundin tsarin mulkin kasar.Babbar Jam’iyyar adawar kasar, United Party for National development ta gabatar da kudirin makon jiya, inda take zargin shugaban da magudin zabe.
Wallafawa ranar:
Kashi daya bisa uku na yan Majalisun kasar 166 suka sanya hannu kan bukatar tsige shugaban.
Sakataren majalisar Garry Nkombo ya shaidawa shugaban masu tsawatarwa a majaisar cewar, saboda muhimmancin kudirin za’a jinkirta mahawarar zuwa watan Yuni lokacin da Majalisar zata koma daga hutu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu