Najeriya
Gobara ta jikkata 'Yan gudun hijira a Najeriya
Rahotanni Daga Jihar Barnon Najeriya, sun ce wasu Yan gudun hijira 14 sun samu raunuka daban daban sakamakon gobarar da ta tashi a sansanonin su da ke dauke da dubban mutane.
Wallafawa ranar:
Talla
Ofishin Jinkai na Majalisar Dinkin Duniya ya sanar da cewar an samu gobarar ne har guda uku, wadda ke zuwa kwanaki bayan irin ta da tayi sanadiyar mutuwar mutane 5.
Har yanzu sansanonin Yan gudun hijira na cike da jama’ar da basu iya komawa garuruwan su ba, saboda rashin cikakken tsaro a kauyukansu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu