Dakarun Masar sun murkushe wani hari a yankin Sinai
A yankin Sinai ,dakarun Masar sun yi nasar kashe wasu mayakan jihadi 14.Sanarwar sojin tace an kashe mutanen ne a lokacin da suka yi kokarin kutsa kai cikin bariqin sojoji dake yankin na Sinai.
Wallafawa ranar:
Mai magana da yahu dakarun Masar ya bayyana cewa sojin kasar 8 ne suka rasa ran su a lokacin da mayakan suka tayar da jigidar bama-bamai .
Wasu rahotani na nuni cewa rundunar sojin kasar ta yi amfani da jirgin sama wajen halaka wasu maharan guda shida.
Ga baki daya sama da mayakan jihadi 100 ne yanzu haka dakarun Masar suka yi nasar halakawa tun bayan da suka kaddamar da yaki da kungiyar Isil a yankin na Sinai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu