Afrika ta Kudu
Cyril Ramaphosa ya dawo gida domin tunkarar boren jama'a
Shugaban Afrika ta Kudu, Cyril Ramaphosa ya katse taron da yake halarta na kasashe renon Ingila a Birtaniya don tinkarar wata mummunar zanga-zanga da ta kunno kai a kasar sa, abin da ake kallo a matsayin daya daga cikin manyan kalubale a sabuwar gwamnatinsa.
Wallafawa ranar:
Talla
Ramaphosa wanda ya dare karagar mulki a cikin watan Fabrairun da ya gabata, ya nuna damuwa matuka kan tarzomar da ta barke a lardin Arewa maso yammacin kasar, in da aka ruwaito cewa, an yi dauki ba dadi tsakanin jami’an ‘yan sanda da masu zanga-zangar nuna bacin rai kan rashin aikin yi da rashawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu