Isa ga babban shafi
ECOWAS

Yammacin Afrika na fuskantar babbar barazana- MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta ce Yankin Afirka ta Yamma na fuskantar babbar barazana sakamakon rikicin da ake samu tsakanin makiyaya da kuma manoma a sassa daban-daban.

Taron wanda ke da nufin tattaunawa kan matsalolin da yammacin Nahiyar ta Afrika ke fuskanta yanzu haka na ci gaba da gudana a Abuja babban birnin Najeriya.
Taron wanda ke da nufin tattaunawa kan matsalolin da yammacin Nahiyar ta Afrika ke fuskanta yanzu haka na ci gaba da gudana a Abuja babban birnin Najeriya. guardian.ng
Talla

Wannan gargadi da Jakadan Majalisar Dinkin Duniya Mohammed ibn Chambas ya karanta a madadin Sakatare Janar Antonio Guterres ya zo ne lokacin bude taron kungiyar kasashen Afirka ta Yamma kan yadda za’a magance matsalar a Abuja.

Guterres ya bukaci daukar matakan gaggawa kan karuwar jama’a da sauyin yanayi da yaduwar makamai da kuma rashin aiwatar da dokokin Yankin da su ke kara matsalar.

Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osibanjo ya bukaci sake nazari kan dokokin ECOWAS domin shawo kan matsalar.

Shugaban gudanarwar kungiyar ta ECOWAS Jean-Claude Kassi Brou ya ce akalla shanu miliyan 60 ake da su a Yankin da ke bukatar wuraren kiwo wanda cigaban da aka samu ke haifar da rikice rikice.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.