Isa ga babban shafi
Najeriya

Mutane 7 sun mutu a harin kunar bakin wake yau a Maiduguri

Rundunar ‘yansandan jihar Borno ta tabbatar da harin kunar bakin waken da wasu mata suka kai wa wasu kauyuka a jihar. Harin na zuwa kwanaki kalilan bayan wani kazamin hari da Boko Haram ta kai masallaci a garin Mubin jihar Adamawa da ya hallaka mutane fiye da 90.

Harin dai ya zo ne kwanaki kalilan bayan makamancinsa a jihar Adamawa wanda ya hallaka kusan mutane casa'in.
Harin dai ya zo ne kwanaki kalilan bayan makamancinsa a jihar Adamawa wanda ya hallaka kusan mutane casa'in. Guardian Nigeria
Talla

Kakakin rundunar DSP Edet Okon ya ce maharani mata ne guda hudu wadanda suka yi damara da bom a jikinsu suka tunkari kauyukan Mainari Kanuri da kuma Shua.

Sanarwar Rundunar ta ce ‘yan kunar bakin waken uku bom din da ke jikinsu ya tashi ne kafin su kai cikin jama’a yayinda dayar kuma ta tayar da bom din tare da hallaka wasu mutane 3 baya jikkata wasu 7.

Rundunar ta ce tuni ta mika gawakinsu ga babban asibitin birnin Maiduguri, yayinda wadanda suka jikkata kuma ke karbar kulawar gaggawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.