Mutanen da Ambaliyar ruwa ta hallaka a gabashin Afrika sun haura 120
Bayan kwashe makonni ana tafka ruwan sama a Yankin Gabashin Afirka da ya dade yana fama da fari, yanzu haka rahotanni sun ce wadanda suka mutu sakamakon ambaliyar da aka samu sun zarce 120, yayin da dubbai suka rasa muhallin su.
Wallafawa ranar:
A kasar Kenya, mutane 120 suka mutu a cikin watanni biyu sakamakon ambaliyar, cikin su harda wasu mutane 8 da gada ta rifta da su daren jiya alhamis.
Wannan yasa kungiyar Red Cross ta bukaci agajin Dala miliyan 5 domin kai musu dauki.
Abbas Gullet, Sakatare Janar na kungiyar Red Cross ya ce gidaje 48,177 suka lalace, abinda ya tilastawa mutane 260,200 rasa matsuguni.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu