Isa ga babban shafi
Sudan

Sama da Mutane miliyan 7 na bukatar agaji a Sudan

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci kara yawan agajin da kasashen duniya ke bai wa Sudan saboda yadda dubban al’ummar kasar ke bukatar taimako sakamakon matsalar tattalin arziki da kuma tabarbarewar al’amura.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce kin bai wa Sudan taimako zai jefa rayuwar mutane akalla miliyan 3 da rabi cikin hadari.
Majalisar Dinkin Duniya ta ce kin bai wa Sudan taimako zai jefa rayuwar mutane akalla miliyan 3 da rabi cikin hadari. AP Photo/Sam Mednick
Talla

Mark Lowcock, shugaban hukumar agaji na Majalisar Dinkin Duniya ya bukaci kungiyoyin agaji da su bada taimakon kusan Dala biliyan daya da rabi domin taimakawa mutane sama da miliyan 7 da ke bukatar agajin.

Tashe tahsen hankulan da ake samu a kasar sun raba miliyoyin mutane da matsugunan su.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce kin bai wa Sudan taimako zai jefa rayuwar mutane akalla miliyan 3 da rabi cikin hadari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.