Sama da Mutane miliyan 7 na bukatar agaji a Sudan
Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci kara yawan agajin da kasashen duniya ke bai wa Sudan saboda yadda dubban al’ummar kasar ke bukatar taimako sakamakon matsalar tattalin arziki da kuma tabarbarewar al’amura.
Wallafawa ranar:
Mark Lowcock, shugaban hukumar agaji na Majalisar Dinkin Duniya ya bukaci kungiyoyin agaji da su bada taimakon kusan Dala biliyan daya da rabi domin taimakawa mutane sama da miliyan 7 da ke bukatar agajin.
Tashe tahsen hankulan da ake samu a kasar sun raba miliyoyin mutane da matsugunan su.
Majalisar Dinkin Duniya ta ce kin bai wa Sudan taimako zai jefa rayuwar mutane akalla miliyan 3 da rabi cikin hadari.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu