Bakonmu a Yau
Abubakar Mairamri kan takaddamar 'yansanda da Bukola Saraki a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:01
Bisa dukkan alamu rikici tsakanin shugaban Majalisar Dattijai na Nigeria Bukola Saraki da Rundunar ‘yan sandan kasar na kara daukan hankulan ‘yan kasar, inda a yau da rana Shugaban Majalisar Dattijan ya nuna zai amsa gayyatar rundunar na kai kansa don amsa tambayoyi dangane da zargin da wasu ‘yan fashi ke yi masa cewa shi ne ubangidansu.A kan haka Garba Aliyu Zaria ya tuntubi Abubakar Mairamri tsohon Kwamishinan ‘yan sanda a jihohin kasar da dama ko takaddamar da ake samu yanzu ba zai gurbata democradiyar yanzu ba.