Isa ga babban shafi

Bakin-haure sama da 40 'yan kasar Habasha sun hallaka

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta majalisar dinkin duniya IOM, ta ce akalla bakin-haure 46 sun rasa rayukansu wasu 16 kuma suka bace, sakamakon nutsewar da suka yi a teku ranar a Laraba.

Jami'an ceto tare da wasu bakin-haure da suka ceto daga teku, yayin da jirginsu ya kife, a lokacin da suke kokarin zuwa kasar Yemen.
Jami'an ceto tare da wasu bakin-haure da suka ceto daga teku, yayin da jirginsu ya kife, a lokacin da suke kokarin zuwa kasar Yemen. AFP/IOM
Talla

Hukumar ta IOM, ta ce baki dayan bakin-hauren 46 ‘yan kasar Habasha ne.

Hadarin ya auku ne yayin da jirgin ruwan da ke safarar bakin-hauren akalla 100 ke kokarin ketara teku zuwa kasar Yemen, bayan barin yankin Bossasso da ke Somalia.

Hukumar kula da ‘yan gudun hijirar ta duniya, ta ce a kowane wata, sama da bakin-haure 7, 000 ke kokarin yin baluguro da ke cike da matukar hadari daga nahiyar Afrika zuwa Yemen, ta hanyar ketara teku.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.