Bakin-haure sama da 40 'yan kasar Habasha sun hallaka
Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta majalisar dinkin duniya IOM, ta ce akalla bakin-haure 46 sun rasa rayukansu wasu 16 kuma suka bace, sakamakon nutsewar da suka yi a teku ranar a Laraba.
Wallafawa ranar:
Hukumar ta IOM, ta ce baki dayan bakin-hauren 46 ‘yan kasar Habasha ne.
Hadarin ya auku ne yayin da jirgin ruwan da ke safarar bakin-hauren akalla 100 ke kokarin ketara teku zuwa kasar Yemen, bayan barin yankin Bossasso da ke Somalia.
Hukumar kula da ‘yan gudun hijirar ta duniya, ta ce a kowane wata, sama da bakin-haure 7, 000 ke kokarin yin baluguro da ke cike da matukar hadari daga nahiyar Afrika zuwa Yemen, ta hanyar ketara teku.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu