Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo

Kotun ICC ta sallami Jean Pierre Bemba

Kotun hukkunta masu manyan laifuka ta duniya ICC, ta sallami Jean Pierre Bemba a yau talata ,Jean Pierre Bemba wanda a can baya ta yankewa hukuncin daurin shekaru 18 bisa aikata laifukan yaki.

Jean-Pierre Bemba Tsohon mataimakin Shugaba Joseph Kabila
Jean-Pierre Bemba Tsohon mataimakin Shugaba Joseph Kabila REUTERS/JERRY LAMPEN
Talla

A shekarar 2016 kotun ta samu Bemba da laifin cin zarafin dan adam, baya ga sauran laifukan yaki, a jamhuriyar Afrika ta Tsakiya a shekarun 2002 da 2003, bisa zarginsa da gazawa wajen hana dakarunsa yi wa fararen hula kisan gilla da kuma aikata fyade.

Sai dai a lokacin da take sanar da soke hukuncin farkon, daya daga cikin alkalan kotun ta ICC, Christine Van den Wijingaert ta ce, alkalai a 2016, sun gaza la’akari da cewa Bemba ya yi iyaka kokarinsa wajen hana aikata laifukan yakin, bayan da aka sanar da shi abinda ke faruwa, dan haka bai kamata a kamashi da laifin da wasu dakarunsa suka aikata ba.

Kungiyar kare hakkin dan adam da Amnesty International ta bayyana sabon hukuncin a matsayin gagarumin koma baya, ga akalla fararen hula 5,000 da suka rayu, bayan cin zarafin da mayakan Jean Pierre Bemba sukai musu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.