Bakonmu a Yau
Magajin garin Gazawa Adamou Waje kan yadda ake tube magadan gari a Jamhuriyar Nijar
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:43
A Jamhuriyar Nijar, ko a cikin makon da ya gabata magadan gari da dama ne aka tube daga mukamansu bisa zargin aikata ba daidai ba a kan ayyukansu.Mafi yawansu dai ana zargin su ne da rashawa ko kuma yin rufda ciki kan dukiyar jama’a, yayin da wasu ke danganta matakin tube magadan garin a matsayin wanda ba ya rasa nasaba da siyasa.Adamou Waje, shi ne magajin garin Gazawa kuma shugaban kungiyar magadan garin reshen jihar Maradi, ya yi bayyana mana yadda yake kallon matakin.