Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sanya hannu kan kasafin kudin shekara ta 2018
Wallafawa ranar:
Kunna - 10:31
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sanya hannu kan kasafin kudin kasar na 2018 bayan share dogon lokaci ana jiya.To sai dai a lokacin da yake rattaba hannu kan kasafin kudin, shugaba Buhari ya bayyana bacin ransa dangane da wasu sauye-sauye da majalisun kasar suka aiwatar dangane da ainihin abin da ya gabatar masu.Sauye-sauyen sun tanadi zaftare makuddan kudade da ya kamata a yi amfani da su domin gudanar da wasu muhimman ayyuka na cigaban kasar, yayin da 'yan majalisar ke cewa sun yi haka bisa tsari na doka. Shirin Kasuwa a Kai Maki Doli na wannan mako, Bashir Ibrahim Idris ya mana dubi ne game da wannan batu.