Cutar Ebola na barazana ga noman Rogo a Afrika
Masu bincike ta fanin noma sun gano wani irin rogo dake dauke da wata cuta da ake kira Ebola Rogo.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A cewar masu binciken wannan cuta za ta fi shafar manoman yammacin Afrika, wanda kuma zai kawo koma baya ga albarkatun noma da manoman yankunan ke samu.
Masu bincinken sun kara da cewa kuma kuda ke yadda kwayar cutar daga itsen rogo zuwa rogo.
Dokta Pita dake aiki da wata hukuma dake ci gaba da gudanar da bincike domin gano maganin wannan cuta ya bayyana cewa matsalar cimaka da ta hafkawa kasar Uganda a shekara ta 1990 da kuma ta hadasa mutuwar mutane kusan 3000 na da nasaba da cutar ebolar Rogo.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu