Isa ga babban shafi
Sudan

Kudirin cirewa Sudan ta kudu takunkumin sayen makamai

Amurka ta gabatar da wani kudiri a gaban kwamitin sulhu na Majalisar dinkin Duniya domin cirewa kasar Sudan ta kudu takunkumin sayen makamai, bayan kasar ta kulla yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin shugaba Salva Kiir da shugaban yan tawaye Riek Machar.

Wasu daga cikin mayakan yan tawayen Sudan ta kudu
Wasu daga cikin mayakan yan tawayen Sudan ta kudu REUTERS/Goran Tomasevic
Talla

Kudirin da wakilin kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya gani, ya bayyana damuwa kan cigaba da samun hare haren da bangarorin ke kaiwa bayan kulla yarjejeniyar zaman lafiyar.

Kasar Amurka ce tafi taimakawa Sudan ta kudu tun bayan samun yancin kan ta daga Sudan a shekarar 2011.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.