Sudan
Kudirin cirewa Sudan ta kudu takunkumin sayen makamai
Amurka ta gabatar da wani kudiri a gaban kwamitin sulhu na Majalisar dinkin Duniya domin cirewa kasar Sudan ta kudu takunkumin sayen makamai, bayan kasar ta kulla yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin shugaba Salva Kiir da shugaban yan tawaye Riek Machar.
Wallafawa ranar:
Talla
Kudirin da wakilin kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya gani, ya bayyana damuwa kan cigaba da samun hare haren da bangarorin ke kaiwa bayan kulla yarjejeniyar zaman lafiyar.
Kasar Amurka ce tafi taimakawa Sudan ta kudu tun bayan samun yancin kan ta daga Sudan a shekarar 2011.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu