Isa ga babban shafi
Senegal

Shugaban China ya fara ziyara a Afrika

A yau asabar shugaban China Xi Jinping ya isa birnin Dakar na kasar Senegal, matakin farko na ziyarar mako daya a wasu uku na nahiyar Afirka.

Shugaba Xi Jinping da kuma Macky Sall, a 2014 a birnin Pékin.
Shugaba Xi Jinping da kuma Macky Sall, a 2014 a birnin Pékin. ROLEX DELA PENA / POOL / AFP
Talla

Wannan ne dai karo na uku da Xi Jinping ke gudanar da ziyara a Afirka a matsayinsa na shugaban kasa, inda bayan ganawa da shugaban Macky Sall a birnin Dakar, zai wuce zuwa birnin Kigali na Rwanda domin ganawa da shugaba Paul Kagame, sannan ya wuce zuwa Afirka ta Kudu domin halartar taron kasashen duniya masu samun habakar tattalin arziki wato Brics a birnin Johanneshurg.

China dai na cigaba da saka jari a kasashen nahiyar Afirka, inda alkaluma ke cewa akwai kamfanoni mallakin ‘yan kasar da yawansu ya haura dubu 10 a sassa daban daban na nahiyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.