Isa ga babban shafi
Najeriya

Mutane 23 sun mutu sakamakon hatsarin kwale-kwale a jihar Sakkwato

A jihar Sakkwato da ke tarayyar Najeriya, mutane 23 ne suka rasa rayukansu a daidai lokacin da suke kokarin tserawa daga wani hari da ‘yan bindiga suka kai wa kauyukansu.

Wani bangare na tafkin Chadi
Wani bangare na tafkin Chadi Shashank Bengali/MCT/MCT via Getty Images
Talla

Mutanen sun hadu da ajalinsu ne lokacin da suke kokarin tsallaka wani kogi ta hanyar amfani da kwale-kwale domin komawa a kauyukansu da suka baro biyo bayan hare-haren da 'yan bindiga suka kai masu a kwanakin da suka gabata.

Lamarin ya faru ne a ranar alhamis, kuma mai magana da yawun rundunar 'yan sanda jihar Sakkwato DSP Codilian Wawei, ta shaida wa wakilinmu Faruk Yabo cewa, adadin mutane da ke cikin kwale-kwalen sun fi 50, kuma hatsarin ya faru ne a gundumar Gandi.

Tuni dai aka tabbatar da mutuwar mutane 23 a cewarta, an kwantar da wasu 8 a asibiti domin samun kulawa jami'an kiwon lafiya yayin da ake cigaba da neman wasu mutane 9.

Bayanai sun 17 daga cikinsu mata ne yayin da sauran 4 yara kanana ne.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.