Isa ga babban shafi
Libya-'Yan cirani

Jami'an Libya sun ceto 'yan cirani 60 daga tekun Mediterranean

Jami’an da ke kula da gabar teku a Libya sun ceto akalla ‘yan ci rani 60 ciki har da mata da kananan yara masu kokarin tsallakawa nahiyar Turai ta Tekun Mediterranean.

Libyan ce dai hanya mafi sauki ga 'yan ciranin da ke son tsallaka nahiyar Turai don samun rayuwa mai inganci.
Libyan ce dai hanya mafi sauki ga 'yan ciranin da ke son tsallaka nahiyar Turai don samun rayuwa mai inganci. REUTERS/Ismail Zitouny
Talla

Kakakin hukumar da ke kula da gabar Tekun a Libya, Ayoub Gassim ya ce ‘yan ciranin da suka kunshi mata 19 da kananan yara 4 sun galabaita a cikin tekun na Mediterranean bayan lalacewar jirginsu a tsakiyar teku tun ranar Litinin.

A cewarsa Tuni suka bayar da kulawar da ta dace ga mutanen su 60 yayinda aka ba su matsuguni a sansanin ‘yan cirani da ke garin Zawiya.

Libya dai na matsayin hanya mafi sauki ga ‘yan ciranin da ke son tsallakawa Nahiyar Turai don samun ingantacciyar rayuwa, yayinda lamarin ya ta’azzara tun bayan hambarar da gwamnatin Mu’ammar Qaddafi a 2011.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.