Isa ga babban shafi
Ghana

Dramani Mahama zai sake tsayawa takarar shugabancin Ghana

Tsohon shugaban Ghana John Dramani Mahama, ya bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takara a zaben shugabancin kasar da za’a yi a cikin shekaru biyu masu zuwa.

Tsohon shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama.
Tsohon shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama. REUTERS/Luc Gnago
Talla

Mahama, wanda ya mulki kasar tsawon shekaru 4 daga 2012 zuwa 2016, ya gaza samun nasara a zaben shugabancin kasar da ya gudana a shekarar ta 2016, wanda abokin hamayyarsa wato shugaba mai ci Nana Akufo-Addo ya lashe.

Tsohon shugaban na Ghana ya bayyana aniyar tasa ce a sakon da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya ce tuni ya mika takardar neman izinin jam’iyyar adawa ta NDC ta tsayar da shi takara.

A tsakanin watan Oktoba zuwa Nuwamba jam’iyyar NDC za ta gudanar da zaben fidda gwani tsakanin masu neman ta basu takarar shugabancin Ghana tsakanin tsohon shugaban kasar, John Dramani Mahama, da kuma sauran masu neman takarar guda 4.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.