Isa ga babban shafi
Libya-Rikici

Kasashen duniya sun yi tir da sabon rikicin Libya

Kasashen Amurka Faransa da kuma Italiya da Birtaniya sun yi tir da rikicin baya-bayan nan da ya barke a Tripoli babban birnin Libya da ya kai ga rasa dimbin rayuka, inda suka bukaci bangarori biyu da ke iko da kasar su dau matakin magance sake faruwarsa.

Yayin fafatawar ta kwanaki biyu an rika ganin yadda bangarorin biyu ke harbawa junansu makaman roka da ya kai ga mutuwar akalla mutane 40.
Yayin fafatawar ta kwanaki biyu an rika ganin yadda bangarorin biyu ke harbawa junansu makaman roka da ya kai ga mutuwar akalla mutane 40. Reuters
Talla

Cikin wata sanarwar hadin gwiwa da kasashen hudu wadda ma’aikatar harkokin wajen Faransa ta fitar ta ce barkewar makamantan rikicin barazana ce ga shirin zaben kasar dama yunkurin dawo da zaman lafiyar da ake yi.

Barkewar sabon rikicin a Tripoli daga ranar Alhamis zuwa daren Juma’a ya hallaka akalla mutane 40 yayinda aka rika ganin makaman roka na keta sararin samaniya matakin da ya tilasta kulle filin jirgin saman kasar guda daya tilo da ke aiki tun bayan yakin basasar 2011.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.