Masar
An gano kauyen da kasa ta binne a Masar
A Masar an gano wani kauye da kasa ta birne wanda ake hasashen cewar ya wanzu ne tun karni na biyar (5 kafin zuwa Annabi Isa alahis Salam. Ma’aikatar al’adu tace wata tawagar masu bincike daga Faransa da Masar suka gano kauyen dake Tel Samara, a arewa maso gabashin kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Ayman Ashmawy, babban jami’in binciken ma’aikatar yace, kafin gano kauyen, babu wani abu makamancin sa da aka gano wadanda akayi amfani da su tsakanin shekarar 4,200 kafin zuwa Annabi Isa alaihis Salam zuwa 2,900.
Yayin tono kauyen an gamu da kasusuwan dabbobi da kuma kayan abinci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu