Isa ga babban shafi
Afrika

Uwargidan Donald Trump na ziyara a kasashen Afrika

Uwargidan shugaban Amurka Donald Trump, wato Melania Trump na ziyara a wasu kasashen nahiyar Afrika da suka hada da Ghana da Malawi da Kenya da kuma Masar.

Uwargidan shugaban Amurka Melania Trump
Uwargidan shugaban Amurka Melania Trump REUTERS/Carlos Barria
Talla

A karon farko kenan da Melania ke gudanar da irin wannan gagarumar ziyara ita kadai, yayin da mai magana da yawunta, Stephanie Grisham ta ce, ziyarar ta ta’allaka akan diflomasiya da kuma jin-kai ga kananan yara.

A makon jiya ne, mai gidanta Donald Trump ya sanar da shirin ziyarar Melania a Afrika, yayin da ya ce, shi da matarsa suna matukar kaunar nahiyar.

Trump ya bayyana Afrika a matsayin wata nahiya mai kayatarwa ta fuskoki da dama.

A can baya, shugaban ya bayyana Afrika a matsayin wani yanki mai cike da kazanta, lamarin da ya janyo masa suka daga bangarori da dama na nahiyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.