Isa ga babban shafi
Najeriya

Atiku na nazarin bai wa Naija Delta damar mamaye dukiyar man yankin

Dan takarar shugabancin kasa a Najeriya a Jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya ce yana tunanin bai wa Yankin Naija Delta izinin mallakar daukacin dukiyar man da ake hakowa sabanin kashi 13 da ake basu.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar kuma dan takarar shugabancin kasa karkashin Jam'iyyar PDP.
Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar kuma dan takarar shugabancin kasa karkashin Jam'iyyar PDP. REUTERS/Tife Owolabi
Talla

A wata hirar da yayi da ‘The Africa Report’ da aka wallafa ranar laraba, Abubakar yace bashi da wata damuwa barin yankin ya mallaki dukiyar da yake da shi, sai dai kawai zai dorawa yankin harajin da zai dinga biya ga gwamnatin tarayya.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana takaicin sa da yadda ake baiwa yankin kashi 13 kacal na arzikin man da ake sayarwa, yayinda a Jamhuriya ta farko kashi 50 ake basu.

Sai dai yace bukatar sa ba za ta samu ba dole sai an sake fasalin dokokin kasar ta hanyar lalama da kuma tattaunawa da sauran jama’a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.