Yan adawar Congo sun shiga tattaunwa a Belgium
Wakilan jam’iyyun adawa a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo sun cigaba da tattaunawa a birnin Brussels na kasar Belgium, domin dinke barakar da ta kunno kai a tsakaninsu dangane da tsayar da Martin Fayulu domin tsayawa takarar shugabacin kasar a zabe mai zuwa.
Wallafawa ranar:
A cikin makon da ya gabata ne ,daukacin yan adawar suka rattaba hannu a yarjejeniyar tsayar da daya daga cikin yan adawa a matsayin dan takara,lamarain da ya harzuka Felix Tshisekedi da ya bukaci ficewa daga cikin kawancen yan adawar kasar.
‘Yan adawa da suka hada da Maurice Katumbi, Adolphe Muzito da kuma Martin Fayulu ne ke halartar tattaunwar, to sai dai jagoran daddiyar jam’iyyar adawar kasar Felix Tshisekedi da kuma Vital Kamerhe sun kaurace masa..
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu