Isa ga babban shafi
Wasanni

Masar da Afrika ta Kudu na takarar karbar bakuncin gasar AFCON

Hukumar kula kwallon kafa ta Afrika CAF, ta ce gasar cin kofin nahiyar dake tafe a 2019 wato AFCON, za ta gudana ne a kasar Masar ko kuma Afrika ta Kudu.

Shugaban hukumar kula da kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF, Ahmad Ahmad.
Shugaban hukumar kula da kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF, Ahmad Ahmad. CRISTINA ALDEHUELA / AFP
Talla

CAF wadda ta bayyana haka a karshen mako, ta ce kasashen guda biyu ne kawai suka mika bukatar neman karbar bakuncin gasar ta AFCON, kafin rufe karbar neman damar daga kasashe a daren ranar Juma’a.

Dukkanin kasashen na Masar ta Afrika ta Kudu sun taba karbar bakuncin gasar kwallon ta nahiyar Afrika sau biyu a baya.

Afrika ta Kudu ta karbi bakuncin gasar ce a shekarun 1996 da kuma 2013 a lokacin da ta maye gurbin Libya.

Masar kuwa ta taba karbar bakuncin gasar ce a shekarar 1986 da 2006.

Rahotanni a baya sun nuna cewa kasashen Ghana, Congo-Brazzaville, da Morocco sun nuna muradin karbar bakuncin gasar sai dai basu bayyana hakan a hukumance ba.

A watan da ya gabata, hukumar ta CAF ta karbe damar da ta baiwa kasar Kamaru na karbar bakuncin gasar, bisa dalilan gaza kammala shirin gine-gine da kuma matsaloli na tsaro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.