Isa ga babban shafi
DR Congo

Kotun Kolin Congo za ta fara sauraron karar zabe

Kotun Kolin Jamhuriyar Dimokirdaiyar Congo ta ce, a ranar Talata za ta fara sauraron karar da dan takarar shugaban kasa Martin Fayulu ya gabatar domin kalubalnatar sakamakon zaben shugaban kasar da ya gudana, in da aka bayyana Felix Tshisekedi matsayin wanda ya samu nasara.

Dan takarar da ya yi na biyu a zaben Congo, Martin Fayulu ya shigar da kara a kotu domin kalubalantar sakamakon zaben shugabancin kasar
Dan takarar da ya yi na biyu a zaben Congo, Martin Fayulu ya shigar da kara a kotu domin kalubalantar sakamakon zaben shugabancin kasar Photo: Stringer/AFP
Talla

Sakataren yada labaran kotun, Baudouin Mwehi ya ce, da misalin karfe 9.30 na safe agogon kasar ne, kotun za ta fara zaman sauraron karar.

Hukumar zabe ta bayyana Tshisekedi a mtsayin wanda ya yi na daya, sai Fayulu a matsayi na biyu, yayin da Emmanuel Ramazani Shadary, dan takarar Jam’iyya mai mulki ya zo na uku.

Kungiyar kasashen da ke kudancin Afrikka sun bukaci sake kidaya kuri’un da kuma kafa gwamnatin hadin kai domin samar da zaman lafiya a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.