Bakonmu a Yau
Alhaji Muhammadu Kiruwa Ardon Zuru kan matakin gwamnatin na koma tsarin baya game da yawon kiwo a sassan kasar
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:35
Gwamnatin Nigeria ta zartas da komawa tsarin baya da manoma za su rika amfani da hanyoyin da suke bi domin tafiya kiwo daga arewacin kasa zuwa kudanci da nufin kawo karshen sabanin da ake samu tsakanin manoma da makiyaya.Matakin na biyo bayan bukatar Ministan gona Audu Ogbe a zaman majalisar tattalin arzikin kasar. Ganin yadda wasu jihohin kasar ke cewa basa son ganin kafar makiyaya a jihohin na su, Garba Aliyu Zaria ya nemi ji daga bakin shugaban Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah na kasar Alhaji Muhammadu Kiruwa Ardon Zuru ina mafita.