Isa ga babban shafi
Majalisar Dinkin Duniya

Dole a kawo karshen cin zarafin masu zanga-zanga a Zimbabwe- MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci gwamnatin Zimbabwe ta kawo karshen, yadda jami’an tsaron kasar ke amfani da karfi fiye da kima kan fararen hular da ke tarzomar adawa da matakin kara farashin man fetur da kashi 150 cikin dari.

Dubban mutane ne dai yanzu haka ke ci gaba da zanga-zanga a sassan kasar ta Zimbabwe don kalubalantar matakin gwamnati na kara farashin man fetur zuwa dalar Amurka 3 ka duk lita guda.
Dubban mutane ne dai yanzu haka ke ci gaba da zanga-zanga a sassan kasar ta Zimbabwe don kalubalantar matakin gwamnati na kara farashin man fetur zuwa dalar Amurka 3 ka duk lita guda. REUTERS/Philimon Bulawayo TPX IMAGES OF THE DAY
Talla

Kididdigar gwamnati ta nuna cewa, mutane uku kawai suka rasa rayukansu a tarzomar, sai dai kungiyoyin kare hakkin dan adam sun ce adadin ya zarta haka sosai.

Majalisar ta yi zargin cewa jami’an tsaron kasar na cin zarafin dan adam hadi da kama daruruwan mutane ba bisa ka’ida.

Kiran na Majalisar Dinkin Duniya ya zo ne bayan da a yau Juma’a, Gwamnatin Zimbabwe ta bada umarnin katse layukan Intanet a ilahirin kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.