Najeriya-Zabe
Ina tunanin yin afuwa ga wadanda suka ci dukiyar kasa - Atiku
Tsohon Mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya bayyana cewar ya na tunanin yi wa mutanen da suka saci dukiyar kasa afuwa domin ganin sun dawo da abinda suka sata suka kuma boye a kasashen ketare.
Wallafawa ranar:
Talla
Abubakar wanda shi ne dan takarar Jam’iyyar PDP a zabe mai zuwa ya bayyana haka ne lokacin da ya ke amsa tambayoyi a wani shiri na musamman domin bayyana shirin da yake da shi ga al’ummar Najeriya.
Atiku Abubakar ya rike mataimakin shugaban kasa a karkashin gwamnatin Olusegun Obasanjo na shekaru 8 tsakanin shekarar 1999 zuwa shekarar 2007.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu