Isa ga babban shafi
Ghana

John Dramani Mahama zai sake tsayawa takarar shugabancin Ghana

Babbar Jam’iyyar adawan Ghana ta NDC ta zabi tsohon shugaban kasar John Dramani Mahama a matsayin wanda zai mata takarar zaben shekara mai zuwa domin fafatawa da shugaba mai ci Nana Akufo-Addo.

Tsohon shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama
Tsohon shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama AFP PHOTO / ISSOUF SANOGO
Talla

Akufo-Addo ne ya kawar da Mahama a karagar mulki a zaben shekarar 2016, sakamakon matsalar tattalin arzikin da kasar ta fuskanta da kuma faduwar farashin man fetur da zinare wanda kasar ta dogara da su.

Kafin dai zaben shekarar 2016, Mahama wanda ya gaji shugaban kasar da ya rasu, ya kada Addo a zaben shekarar 2012.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.