Isa ga babban shafi
Libya

Libya: An azabtar da 'yan ci rani a sansanin karkashin kasa

Rahotanni daga Libya sun ce 'yan ci rani akalla 30 da ke son tsallakawa Turai ciki har da kananan yara, sun fuskanci azabtarwa a wani sansanin karkashin kasa, saboda yunkurin da suka yi na tserewa daga inda ake tsare da su.

Wasu 'yan ci rani da ke kokarin ketara teku zuwa nahiyar turai, da mayakan sa kai na Libya ke tsare da su a sansanoni.
Wasu 'yan ci rani da ke kokarin ketara teku zuwa nahiyar turai, da mayakan sa kai na Libya ke tsare da su a sansanoni. Reuters
Talla

Akalla bakin-haure 150 ne suka balle daga sansanonin da mayaka masu iko da yankunan Libya ke tsare da su, da nufin rugawa zuwa hukumar yaki da safarar bakin-haure ta kasar.

Wani shaidar gani da ido ya ce kafin yukurin tserewa, sai da bakin-hauren suka yi zanga-zangar nuna bacin rai kan munin yanayin sansanonin da aka tsare su.

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar dinkin duniya, tace mafi akasarin bakin-hauren da ake tsare dasu a Libya a yanzu, wadanda kasashen Turai suka maido kasar ne, bayan da sukai yunkurin ketara takun Mediterranean zuwa nahiyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.