Isa ga babban shafi
Afrika

Rwanda ta gayyaci Emmanuel Macron

Kasar Rwanda ta gayyaci shugaban Faransa Emmanuel Macron da ya halarci bikin tunawa da mutane sama da 800,000 da aka kashe a kisan kiyashin da ya biyo bayan yakin basasar kasar a shekarar 1994.

Paul Kagame, Shugaban kasar Rwanda
Paul Kagame, Shugaban kasar Rwanda © AFP
Talla

Karamin ministan harkokin wajen kasar, Olivier Nduhungirehe yace an gayyaci Macron bikin da za’ayi ranar 7 ga watan gobe, gayyatar dake zuwa a matse.

Rwanda ta dade tana zargin Faransa da goyan bayan gwamnatin Hutu da kuma horar da sojojin ta da yan tawayen su da suka aikata kisan kan yan kabilar Tutsi.

Shugaba Macron da yanzu haka ke ziyarar kasashen Djibouti da Habasha da Kenya bai bayyana ko zai amsa gayyatar ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.