Sai 13 ga Aprilu za a sake zaben Gwamnan jihar Rivers- INEC
Hukumar zaben Najeriya INEC ta tsayar da ranar 13 ga watan Afrilu, a matsayin ranar da za ta sake gudanar da zaben Gwamna da na ‘Yan Majalisun Jihar Rivers, bayan soke kuri’u da dama da aka kada yayin zaben da ya gabata a ranar 9 ga watan Maris.
Wallafawa ranar:
Festus Okoye, babban jami’in lura da sashin wayar da kan masu kada kuri’a da yada labaran hukumar ta INEC, ya ce a ranar 2 ga watan Afrilu zuwa 5 ga watan, za a ci gaba da kidayar kuri’un da aka kada a zabukan na baya, aikin da aka dakatar saboda rikicin siyasa.
Hukumar zaben Najeriyar dai ta dakatar da tattara sakamakon zaben na Gwamnan jihar Rivers ne bayan tashe-tashen hankulan da aka fuskanta yayin zaben na ranar 9 ga wata.
Tun a wancan lokaci dai matakin na INEC ya haddasa zanga-zanga bisa zargin hukumar zaben na hada baki da jam'iyya mai mulki a Najeriyar APC don murde sakamakon zabe.
A ranar Asabar mai zuwa ne dai hukumar ta INEC za ta gudanar da zabe a yankunan da aka gaza kammala zaben Gwamna cikin jihohin kasar 6 ciki har da Kano da Bauchi da kuma Sokoto.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu