Mutane 60 sun mutu sakamakon hadarin mota a Ghana
Akalla mutane 60 ne suka rasa rayukansu sakamakon hadarin da wasu motocin daukar fasinja biyu suka yi yankin Bono da ke kudu maso gabashin kasar Ghana.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Mai magana da yawun ‘yan sandan kasar ta Ghana Joseph Antwi Gyawu, ya ce motocin sun yi taho mu-gama ne da misalin karfe biyu na daren da ya gabata.
Bayanai sun ce bayan da motocin suka yi taho mu-gama, nan take daya daga cikinsu ta kama da wuta, a lokacin kowace mota na dauke da fasinjoji 50 a cikinta.
Kwame Arhin, likita a asibitin gwamnati da ke garin Kintampo kusa da inda lamarin ya faru, ya ce yanzu haka akwai mutane 28 da aka kwantar a asibitin don kula da su sakamakon raunukan da suka samu.
A shekara ta 2016, wata motar fasinja ta yi taho mu gama da wata motar daukar kaya a kan hanyar Tamale, inda mutane 53 suka rasa rayukansu
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu