Isa ga babban shafi
Faransa-Rwanda

Macron ba zai halarci taron juyayin kisan kiyashin Rwanda ba

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ba zai halarci taruruka da addu’o’in cika sekaru 25 da barkewar kisan kiyashin kasar Rwanda da za a yi ranar 7 ga watan afrilu mai zuwa ba.

Kasusuwan mutnen da aka hallaka a kisan kiyashin Rwanda
Kasusuwan mutnen da aka hallaka a kisan kiyashin Rwanda Reuters
Talla

Sakamakon kusancin da aka samu tsakanin Faransa da Rwanda bayan zuwan Macron karagar mulki, wannan ya sa gwamnatin Rwanda aike wa shugaban da goron gayyata domin ya halarci wadannan adu’o’I da za a yi a birnin Kigali, to sai Macron ya ce zai tura wani dan majalisar dokokin kasar mai suna Hervé Berville domin ya wakilce shi.

Hervé Berville maraya ne da ya tsira daga kisan kiyashin da aka yi 1994, kafin dauke shi zuwa Faransa lokacin yana da shekaru 4 a duniya.

Shugaban Rwanda Paul Kagame ya share tsawon shekaru yana takun-saka da mahukuntan Faransa, bisa zargin cewa suna da hannu a wannan rikici da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane dubu 800 mafi yawansu ‘yan kabilar Tutsi marasa rinjaye a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.