Isa ga babban shafi
Faransa-Ta'addanci

Sojin Faransa sun hallaka 'yan ta'adda 30 akan iyakar Mali da Burkina Faso

Rundunar sojin Faransa ta ce dakarunta da hadin gwiwar na kasar Mali sun yi nasarar hallaka mayakan jihadi fiye da 30 yayin wani gumurzu tsakaninsu cikin makon jiya a gab da kan iyakar Mali da Burkina Faso.

Sojin Faransa a Mali
Sojin Faransa a Mali REUTERS/Eric Gaillard
Talla

Sanarwar rundunar sojin ta Faransa ta ce tun a ranar 2 ga watan nan ne dakarun na ta suka kaddamar da farmakin kan 'yan ta'addan masu ikirarin jihadi, harin da ya haifar da gagarumar koma baya a tsare-tsaren 'yan ta'addan.

Yayin Farmakin na makon jiya, wani likitan sojin na Faransa ya rasa ransa sanadiyar taka nakiya da motarsu ta yi a yankin Gurma da ke tsakiyar gabashin Mali.

A jimilce da dakarun rundunar sojan Faransa Barkhane 700 da sojan Mali 150 ne aka tanada a aikin, da ya fara daga sansanin sojan Mali da ke Hombori mai tazarar kilomita 80 arewacin kan iyakar kasar da Burkina Faso.

Kakakin sojin Faransa Kanal Patrik Steiger, ya ce a bangaren Burkina Faso an saka sojan kasar cikin shiri domin hana kutsen 'yan ta'addan daga kudanci kasar,

Bayan share tsawon shekara daya da rabi na fada da masu ikararin Jihadi a yankin Liptako, dake hannun riga da yankunan (nord-est) mali, runduna sojan Barkhane ta kara matsa kaimi wajen fadada ayukanta a wannan sabon yanki, da ke makwabtaka da yankunan kasar Mali uku (Gao, Tombouctou da kuma Mopti) da suka hada iyaka da Burkina Faso.

A baya bayan nan, sojan Faransa suka sake kafa wani sansani a wajen garin Gossi mai tazarar kilo mita 150 yammacin Gao da ke arwacin Mali.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.