Isa ga babban shafi
Sudan

Uganda na son bai wa al-Bashir na Sudan mafaka

Uganda ta ce a shirye take ta bai wa tsohon shugaban kasar Sudan, Omar Hassan al Bashir mafakar siyasa bayan kifar da gwamnatinsa.

Omar Hassan al-Bashir na Sudan na garkame a gidan yarin Khartoum
Omar Hassan al-Bashir na Sudan na garkame a gidan yarin Khartoum REUTERS/Mohamed Nureldin Abdallah
Talla

Karamin Ministan Harkokin Wajen Uganda, Henry Okello Oryem ya ce, muddin aka gabatar da bukatar bai wa al-Bashir mafaka ga kasar, shugabanninta za su duba bukatar da kuma amincewa da ita.

Ministan ya ce, tsohon shugaban ya taka gagarumar ruwa wajen sasanta rikicin Sudan ta Kudu, saboda haka bai ga dalilin da zai sa Uganda ta hana shi mafaka ba.

Rahotanni daga Sudan sun ce, sojojin da ke mulkin kasar a yanzu, sun tasa keyar tsohon shugaban zuwa gidan yarin Kober da ke birnin Khartoum, kamar yadda iyalansa suka bayyana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.