Mutane sun mutu a hadarin kwale-kwale
Rahotanni daga Janhuriyar Democradiya Congo na cewa an sake samun kifewar wani kwale-kwale, in da nan take mutane 37 suka mutu. Wannan na zuwa ne mako daya bayan da aka samu irin wannan hadari da ya salwantar da rayukan mutane masu yawa.
Wallafawa ranar:
Gawarwaki 16 daga cikin mamatan, an tsamo su ne a daidai wurin da kwale-kwalen ya kife a kogin gabashin kasar, kamar dai yadda Gwamnan yankin Papy Omeonga Tchopa ya tabbatar.
Kamar yadda yake cewa, musabbabin hadarin abubuwa biyu ne, na farko matukin kwale-kwalen sai da ya yi mankas da barasa, sannan kuma kwale-kwalen ya kwaso mutane da kaya da suka wuce kima.
Mako daya kenan da samun samun irin wannan hadari a kogin Kivu a lokacin da mutane 130 suka salwanta.
Wannan al'amari yasa shugaban kasar Felix Tshekedi ware ranar Juma'a da ta gabata domin zaman makoki a fadin kasar.
Masana sun ce, ana samun mamata ne a irin wannan hatsari saboda yawanci masu shiga kwale-kwalen basa amfani da rigunan kare tsautsayi
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu