Isa ga babban shafi
Ghana

Ghana ta zama kasa ta 2 da ta kaddamar da rigakafin cutar Malaria

Kasar Ghana ta kaddamar da shirin yiwa yara rigakafin kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro ko kuma malaria, a karkashin wani gagarumin shirin da aka kaddamar domin yaki da cutar a duniya.

Misalin yadda sauro ke sanyawa dan adam cutar Malaria ta hanyar cizo.
Misalin yadda sauro ke sanyawa dan adam cutar Malaria ta hanyar cizo. AFP/PHILIPPE HUGUEN
Talla

Masu aikin bada rigakafin sun fara bada shi ne ga mutanen da suka fi kowa barazanar kamuwa da cutar da suka hada da mata da jarirai a garin Cape Coast dake da nisan kilomita 150 daga birnin Accra.

Wani likita, Justice Arthur ya bayyana fatar sa na ganin maganin rigakafin ya taimaka wajen dakile yadda cutar ke haddasa rasa rayuka a kasar.

An dai zabi Ghana da Kenya da Malawi ne domin gwajin maganin rigakafin a nahiyar Afirka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.