Bakonmu a Yau
Issiakou Ibrahim Madougou kan rikicin siyasar kasar Benin
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:29
Jami’an tsaro a Jamhuriyar Benin sun yi amfani da harsashen gaske domin tarwatsa magoya bayan ‘yan adawa da suka taru a harabar gidan tsohon shugaban kasar Boni Yayi.Kamfanin dillancin labarai na Faransa AFP ya tabbatar da mutuwar akalla mutane uku, sakamakn harbin su da bindiga, yayin da bayanai ke cewa matasa sun ci gaba da farfasa kadarori da kuma kone kone musamman a birnin Cotonou.Domin jin halin da ake ciki, Ahmed Abba ya tuntubi Alhaji Issiakou Ibrahim Madougou, wanda yanzu haka ke birnin Cotonou.