Sudan: Sojoji sun jikkata masu zaman dirshan da dama a Khartoum
Mutane da dama sun jikkata a Sudan, sakamakon bude musu wuta da ake zargin wasu sojoji sun yi a yau Laraba, yayinda suke gudanar da zaman dirshan a babban birnin kasar Khartoum.
Wallafawa ranar:
Wani shaidar gani da ido, Mohammed Dahab ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa, lamarin ya auku ne a lokacin da masu zanga-zangar suka yi dandazo a gaf da harabar hedikwatar rundunar sojin kasar da ke tsakiyar birnin Khartoum.
Zaman dar dar a kasar ta Sudan ya sake bayyana ne a dai dai lokacin da ake sa ran soma tattaunawa tsakanin wakilan gwamnatin sojoji mai rikon kwarya, da kuma bangaren farar hula da suka jagoranci, zanga-zangar da ta kawo karshen mulkin tsohon shugaban kasar ta Sudan Omar al-Bashir.
A baya bayan nan dai Sojoji da kuma jagororin masu zanga-zangar neman sauyi a Sudan suka cimma yarjejeniyar kafa gwamnatin riko wadda za ta share tsawon shekaru uku kafin shirya sabbin zabubuka a kasar.
Janar Yasser Atta, mamba a majalisar koli ta mulkin sojin kasar ne ya sanar da kulla wannan yarjejeniya bayan share tsawon kwanaki ana tattaunawa tsakanin bangarorin biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu