Najeriya
Shirin bunkasa noman rani a jihar Kano da Ke Najeriya
Gwamnatin Najeriya ta kaddamar da wani bincike da zai lakume makudan kudade domin kawar da wasu sinadarai na kanwa da gishiri da ke barazana ga gonakin noman rani a Jihar Kano da ke arewacin Kasar.Aikin binciken ya biyo bayan korafe-korafen da manoma ke yi dangane da illar wadannan sanadarai ga amfanin gona, wanda suka ce al’amarin ya tasamma zama barazana ga yunkurin samar da wadataccen abinci a kasar.Wakilinmu na Kano Abubakar Abdulkadir Dangambo ya aiko mana rahoto a game da wannan shiri.
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:03