Isa ga babban shafi

Mutane da Ebola ta kashe a Congo sun haura dubu 1 da dari 5

Ma’aikatar lafiya a Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo ta sanar da karuwar mutanen da suka rasa rayukansu sanadiyyar annobar cutar Ebolar da kasar ke fuskanta.

Yadda ake shirin binne wani da Cutar Ebola ya hallaka a yankin Butembo na Dimokradiyyar Congo ranar 26 ga watan Maris 2019.
Yadda ake shirin binne wani da Cutar Ebola ya hallaka a yankin Butembo na Dimokradiyyar Congo ranar 26 ga watan Maris 2019. REUTERS/Baz Ratner
Talla

Cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar, ta nuna cewa adadin mutanen da cutar ta hallaka ya karu zuwa mutum dubu 1 da 506 daga watanni goma baya zuwa ranar  Lahadi yayinda yanzu haka ake da mutane dubu 2 da 239 da ke fama da cutar.

Ko cikin watan Yunin nan dai akalla wasu iyalai 2 sun rasa rayukansu a Uganda bayan ziyartar ‘yan uwansu a kasar ta Demokradiyyar Congo.

Kawo yanzu dai akalla mutane dubu 141 aka yiwa rigakafin cutar ta Ebola baya ga jami’an lafiya galibi a yankin gabashin kasar da nan ne annobar cutar ta fi tsananta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.