Isa ga babban shafi
Libya

Mutane dubu 1 sun halaka a sabon yakin Libya

Kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya, ya bukaci tsagaita wutar yakin da ake fafatwa a Libya, tsakanin sojin gwamnatin Fayez Al-Sarraj da kasashen duniya ke marawa baya, da dakarun Janar Khalifa Haftar mai rike da yankin gabashin kasar.

Wasu yan gudun hijira daga kasashen Afirka, zaune a harabar sansanin Tajoura dake Tripoli, da jiragen yaki suka kaiwa farmaki. 2/7/2019.
Wasu yan gudun hijira daga kasashen Afirka, zaune a harabar sansanin Tajoura dake Tripoli, da jiragen yaki suka kaiwa farmaki. 2/7/2019. Reuters
Talla

Kiran na majalisar dinkin duniya ya zo ne bayan da adadin mutane dubu daya suka halaka, a dalilin sabon yakin da aka shafe watanni uku ana gwabzawa, a kokarin da Haftar ke yin a kwace iko da birnin Tripoli, hedikwatar gwamnatin ta Libya.

Wani rahoto da hukumar lafiya ta duniya WHO ta fitar, ya nuna cewa, akalla mutane dubu 5 yakin ya jikkata, wasu sama da dubu 100 kuma suka tsere daga muhallansu, bayaga bayaga hasarar rayuka dubu guda.

A ranar talata, 2 ga watan Yuli, wani farmakin jiragen yaki kan sansanin Tajoura dake birnin Tripoli, ya halaka 'yan gudun hijira 53, wanda tuni gwamnatin Al-Sarraj ta dora alhakin kan dakarun Janar Haftar, zargin da ya musanta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.