Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojojin hadin gwiwa sun dakile harin Boko Haram

Rundunar hadin gwiwa ta kasashen Najeriya da Nijar da Kamaru da kuma Chadi, tayi nasarar dakile wani hari da mayakan kungiyar Boko haram ta yi yunkurin kaiwa a Baga.

Wasu dakarun sojin Najeriya.
Wasu dakarun sojin Najeriya. AFP
Talla

Mai Magana da yawun rundunar, Kanal Timothy Antigha yace mayakan sun yi kokarin tafka barnar ce da misalin karfe 5.30 na asuba, inda dakarun dake aiki a garin suka murkushe su.

Kanal Antigha ya ce dakarun hadin gwiwar sun samu nasarar halaka 10 daga cikin mayakan na Boko Haram, daga cikinsu kuma harda ‘yan kunar bakin guda 4.

Yunkunrin farmakin na baya bayan nan, ya zo ne kasa da mako daya, bayan da mayakan na Boko Haram suka halaka sama da mutane 60 yayinda suke gudanar da jana’iza a Jihar Borno.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.