Isa ga babban shafi
Afrika

Guterres ya roki yan tawayen ADF

Sakataren majalisar dinkin duniya Antonio Guterresh, da ya soma ziyarar kwanaki uku a Jamhuriyar Congo ya roki mayakan kungiyar yan tawayen ADF da su yiwa Allah sun ajiye makamai.

Yan tawayen ADF a kasar Congo
Yan tawayen ADF a kasar Congo John WESSELS / AFP
Talla

Guterres ya soma ziyarar a ne garin Goma, babban birnin lardin arewacin Kivu.

Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya roke su da su bayar da hadin kai don tabbatar da zaman lafiya a wannan yanki da kasar baki daya.

A karshe Antonio Gutteres ya yi kira ga jami’an kiwon lafiya tareda yaba musu dangane da jajircewar su wajen yaki da cutar Ebola.

A dai-dai lokacin da Guterres ke ziyarar kasar ,Ministan tsaron kasar ya fitar da wasu alkaluma dake bayyana adadin sojan kasar da suka rasa rayukan su a yaki da kungiyar ADF,akala sojoji 1662 suka mutu a yakin da kasar ke yi da yan ADF kama daga shekara  ta 2014.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.