Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojin Najeriya sun dakile harin Boko Haram a Jami'ar Maiduguri

Rahotanni daga Najeriya sun ce rundunar sojin kasar ta yi nasarar dakile wani harin ta'addanci da kungiyar Boko Haram ta shirya kai wa Jami'ar Maiduguri cikin daren jiya Lahadi, inda aka rika jin karar harbe-harbe a makarantar.

Wasu Sojin Najeriya
Wasu Sojin Najeriya AFP
Talla

Majiyoyi daga makarantar sun ce an kusan sa'a guda da rabi ana jiyo karar harbin indiga da ke nuna musayar wuta tsakanin Sojin da mayakan na Boko Haram, kafin daga bisani al'amura su daidaita.

Rahotanni sun ce wasu daliban makarantar da ke jarabawa sun yi kokarin barin makarantar cikin dare domin tsira da rayukansu.

Ko a jiya akwai wasu labarai da jaridun Najeriyar suka wallafa wanda ke nuna yadda harin na Boko Haram ya hallaka Sojin kasar 13.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.